Suratul Yaseen Tare Da Fassarar Hausa

Fassarar suratu Yaseen yana da tasirin ruhi da ruhi da yawa akan rayuwar dan adam. Suratun Yaseen ita ce sura ta 36 a cikin Alkur’ani mai girma, kuma tana a mataki na 22 da 23 na Alkur’ani. Ta hanyar karanta fassarar wannan sura za a iya kara musu ilimi da kuma kara fa’ida. Yana taimakawa wajen fahimtar saƙo mai tsarki wanda ke ba da shiriya da bayyanawa ga dukkan musulmi. Yana bayar da darussa na ɗabi’a da ɗabi’a.

Karatun suratun Yaseen na ayoyi 83 na iya kawo kwanciyar hankali da kwanciyar hankali, musamman a lokacin damuwa. Ana samun fassarar suratu Yaseen a cikin yaruka 95+. Musulmai da yawa suna jin natsuwa wajen karanta surar da harshen larabci, amma domin fahimtar cikakkiyar ma’anar wannan sura, kowane Musulmi ya kamata ya karanta cikakkiyar fassarar Surah Yaseen a rayuwarsa. Zaku iya sauke surar Yaseen cikakkin PDF cikin harshen Hausa. Yana da sauƙi masu karatu su karanta suratu Yaseen akan layi ta hanyar zazzage fayil ɗin su adana shi zuwa na’urorinsu don saurin shiga.

Saurari Surah Yaseen Sauti cikin Hausa

Karanta Cikakkun Suratun Yaseen tare da Fassarar Hausa Online

36.1

يسٓ

Y. S̃.ا

Tafseer

Tafseer

36.0

بِسۡمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحۡمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.ا

Tafseer

Tafseer

36.3

إِنَّكَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Lalle kai, haƙĩƙa kanã cikinManzanni.ا

Tafseer

Tafseer

36.2

وَٱلۡقُرۡءَانِ ٱلۡحَكِيمِ

Inã rantsuwa da Al- ƙur'ãni Mai hikima.ا

Tafseer

Tafseer

36.5

تَنزِيلَ ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

( Allah Ya saukar da Al- kur'ãni ) saukarwar Mabuwãyi, Mai jin ƙai.ا

Tafseer

Tafseer

36.4

عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

A kan hanya madaidaiciya.ا

Tafseer

Tafseer

36.7

لَقَدۡ حَقَّ ٱلۡقَوۡلُ عَلَىٰٓ أَكۡثَرِهِمۡ فَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Lalle, haƙĩƙa, kalma tã wajaba a kan mafi yawansu, dõmin sũ, bã zã su yi ĩmãni ba.ا

Tafseer

Tafseer

36.6

لِتُنذِرَ قَوۡمٗا مَّآ أُنذِرَ ءَابَآؤُهُمۡ فَهُمۡ غَٰفِلُونَ

Dõmin ka yi gargaɗi ga waɗansu mutãne da ba a yi gargaɗi ga ubanninsu ba, sabõda haka sũmasu rafkana ne.ا

Tafseer

Tafseer

36.9

وَجَعَلۡنَا مِنۢ بَيۡنِ أَيۡدِيهِمۡ سَدّٗا وَمِنۡ خَلۡفِهِمۡ سَدّٗا فَأَغۡشَيۡنَٰهُمۡ فَهُمۡ لَا يُبۡصِرُونَ

Kuma Muka sanya wata tõshiya a gaba gare su, da wata tõshiya a bãyansu, sabõda haka Muka rufe su, sai suka zama bã su gani.ا

Tafseer

Tafseer

36.8

إِنَّا جَعَلۡنَا فِيٓ أَعۡنَٰقِهِمۡ أَغۡلَٰلٗا فَهِيَ إِلَى ٱلۡأَذۡقَانِ فَهُم مُّقۡمَحُونَ

Lalle Mũ, Mun sanya ƙuƙumma a cikin wuyõyinsu, sa'an nan sũ ( ƙuƙumman sun kai ) har zuwa ga haɓõɓinsu, sabõda haka, sũ banƙararru ne.ا

Tafseer

Tafseer

36.11

إِنَّمَا تُنذِرُ مَنِ ٱتَّبَعَ ٱلذِّكۡرَ وَخَشِيَ ٱلرَّحۡمَٰنَ بِٱلۡغَيۡبِۖ فَبَشِّرۡهُ بِمَغۡفِرَةٖ وَأَجۡرٖ كَرِيمٍ

Kanã yin gargaɗi kawai ga wanda ya bi Alƙur'ãni ne, kuma ya ji tsõron mai rahama a fake. To, ka yi masa bushãra da gãfara da wani sakamako na karimci.ا

Tafseer

Tafseer

36.10

وَسَوَآءٌ عَلَيۡهِمۡ ءَأَنذَرۡتَهُمۡ أَمۡ لَمۡ تُنذِرۡهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Kuma daidai yake a gare su, shin, ka yi musu gargaɗi kõ ba ka yi musu gargaɗi ba, sũ bã zã su yi ĩmãni ba.ا

Tafseer

Tafseer

36.13

وَٱضۡرِبۡ لَهُم مَّثَلًا أَصۡحَٰبَ ٱلۡقَرۡيَةِ إِذۡ جَآءَهَا ٱلۡمُرۡسَلُونَ

Ka ba su, misali, labarin mutanen ƙauyawa a lokacin da Manzanni suka je mata.ا

Tafseer

Tafseer

36.12

إِنَّا نَحۡنُ نُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰ وَنَكۡتُبُ مَا قَدَّمُواْ وَءَاثَٰرَهُمۡۚ وَكُلَّ شَيۡءٍ أَحۡصَيۡنَٰهُ فِيٓ إِمَامٖ مُّبِينٖ

Lalle ne Mu, a wata rãnar da Muke tãyar da matattu. Lalle ne Mũ, Munã rubũta abin da suka aikata, kuma da abin da suka bari a bãyansu, Munã kiyaye kõwane abu a cikin Littafi bayyananne.ا

Tafseer

Tafseer

36.15

قَالُواْ مَآ أَنتُمۡ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا وَمَآ أَنزَلَ ٱلرَّحۡمَٰنُ مِن شَيۡءٍ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا تَكۡذِبُونَ

Sai mutanen suka ce: Ba ku zama ba face mutane misãlanmu, kuma Allah Mai rahama bai saukar da kõme ba: ƙarya kuke faɗa.ا

Tafseer

Tafseer

36.14

إِذۡ أَرۡسَلۡنَآ إِلَيۡهِمُ ٱثۡنَيۡنِ فَكَذَّبُوهُمَا فَعَزَّزۡنَا بِثَالِثٖ فَقَالُوٓاْ إِنَّآ إِلَيۡكُم مُّرۡسَلُونَ

A lõkacin da Muka aika ( Manzannin ) biyu zuwa gare su, sai suka ƙaryata su, sa'an nan Muka ƙarfafa ( su ) da na uku, sai suka ce: « Lalle mũ, Manzanni ne zuwa gare ku. »ا

Tafseer

Tafseer

36.17

وَمَا عَلَيۡنَآ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُ ٱلۡمُبِينُ

« Kuma bãbu abin da ke kanmu, fãce iyar da manzanci bayyananne. »ا

Tafseer

Tafseer

36.16

قَالُواْ رَبُّنَا يَعۡلَمُ إِنَّآ إِلَيۡكُمۡ لَمُرۡسَلُونَ

Suka ce: « Ubangijinmu Yã sani, lalle mũ, haƙiƙa Manzanni nezuwa gare ku. »ا

Tafseer

Tafseer

36.19

قَالُواْ طَـٰٓئِرُكُم مَّعَكُمۡ أَئِن ذُكِّرۡتُمۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ مُّسۡرِفُونَ

Sai manzanni suka ce: « Shu'umcinku, yanã tãre da ku. Ashe, dõmin an tunãtar da ku? Ã'a, kũ dai mutãne ne mãsu ƙẽtare haddi.»ا

Tafseer

Tafseer

36.18

قَالُوٓاْ إِنَّا تَطَيَّرۡنَا بِكُمۡۖ لَئِن لَّمۡ تَنتَهُواْ لَنَرۡجُمَنَّكُمۡ وَلَيَمَسَّنَّكُم مِّنَّا عَذَابٌ أَلِيمٞ

Jama'a suka ce, “Mun ɗauke ku a matsayin mugun abu. Idan ba ku hanu ba (daga wannan) za mu jefe ku, kuma za ku sami azãba mai raɗaɗi daga gare mu.ا

Tafseer

Tafseer

36.21

ٱتَّبِعُواْ مَن لَّا يَسۡـَٔلُكُمۡ أَجۡرٗا وَهُم مُّهۡتَدُونَ

« Ku bi waɗanda bã su tambayar ku wata ijãra kuma sũ shiryayyu ne. »ا

Tafseer

Tafseer

36.20

وَجَآءَ مِنۡ أَقۡصَا ٱلۡمَدِينَةِ رَجُلٞ يَسۡعَىٰ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱتَّبِعُواْ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma wani mutum daga mafi nĩsan birnin ya je, yanã tafiya da gaggãwa, ya ce: « Ya mutãnẽna! Ku bi Manzannin nan. »ا

Tafseer

Tafseer

36.23

أَأَتَّخِذُ مِنْ دُونِهِ آلِهَةً إِنْ يُرِدْنِ الرَّحْمَٰنُ بِضُرٍّ لَا تُغْنِ عَنِّي شَفَاعَتُهُمْ شَيْئًا وَلَا يُنْقِذُونِ

« Shin, zan riƙi waninSa abũbuwan bautãwa? Idan Mai rahama Ya nufe ni da wata cũta, to cẽtonsu bã ya amfanĩna da kõme, kuma bã za su iya tsãmar da ni bã. »ا

Tafseer

Tafseer

36.22

وَمَا لِيَ لَآ أَعۡبُدُ ٱلَّذِي فَطَرَنِي وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

« Kuma mene ne a gare ni, bã zan bauta wa Wanda Ya ƙãga halittata ba, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku? »ا

Tafseer

Tafseer

36.25

إِنِّي آمَنْتُ بِرَبِّكُمْ فَاسْمَعُونِ

« Lalle ni, nã yi ĩmãni da Ubangijinku, sabõda haka ku saurãre ni. »ا

Tafseer

Tafseer

36.24

إِنِّي إِذًا لَفِي ضَلَالٍ مُبِينٍ

Idan na yi haka, zan shiga cikin kuskure bayyananne.ا

Tafseer

Tafseer

36.27

بِمَا غَفَرَ لِي رَبِّي وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُكْرَمِينَ

«Game da gãfarar da Ubangijjĩna ya yi mini, kuma Ya sanya ni a cikin waɗanda aka girmama. »ا

Tafseer

Tafseer

36.26

قِيلَ ادْخُلِ الْجَنَّةَ ۖ قَالَ يَا لَيْتَ قَوْمِي يَعْلَمُونَ

Aka ce ( masa ) , « Ka shiga Aljanna. » Ya ce, « Dã dai a ce mutãnẽna sunã iya sani. »ا

Tafseer

Tafseer

36.29

إِنْ كَانَتْ إِلَّا صَيْحَةً وَاحِدَةً فَإِذَا هُمْ خَامِدُونَ

Ba ta kasance ba face tsawa guda, kuma duk sun bace.ا

Tafseer

Tafseer

36.28

وَمَا أَنْزَلْنَا عَلَىٰ قَوْمِهِ مِنْ بَعْدِهِ مِنْ جُنْدٍ مِنَ السَّمَاءِ وَمَا كُنَّا مُنْزِلِينَ

Kuma ba Mu saukar da waɗansu runduna ba daga sama a kan ( halaka ) mutãnensa, daga bãyansa, kuma bã zã Mu kasance. kuma ba a wajabta mana ba.ا

Tafseer

Tafseer

36.31

أَلَمْ يَرَوْا كَمْ أَهْلَكْنَا قَبْلَهُمْ مِنَ الْقُرُونِ أَنَّهُمْ إِلَيْهِمْ لَا يَرْجِعُونَ

Ba su gani ba, da yawa Muka halakar da ( mutãnen ) ƙarnõni a gabãninsu kuma cẽwa su bã zã su kõmo ba?ا

Tafseer

Tafseer

36.30

يَا حَسْرَةً عَلَى الْعِبَادِ ۚ مَا يَأْتِيهِمْ مِنْ رَسُولٍ إِلَّا كَانُوا بِهِ يَسْتَهْزِئُونَ

Yã nadãma a kan bãyĩNa! Wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu yi masa izgili.ا

Tafseer

Tafseer

36.33

وَآيَةٌ لَهُمُ الْأَرْضُ الْمَيْتَةُ أَحْيَيْنَاهَا وَأَخْرَجْنَا مِنْهَا حَبًّا فَمِنْهُ يَأْكُلُونَ

Kuma ãyã ce a gare su: Ƙasã matacciya, Mu rãyar da ita, Mu fitar da ƙwãya daga gare ta, sai gã shi daga gare ta suke ci.ا

Tafseer

Tafseer

36.32

وَإِنْ كُلٌّ لَمَّا جَمِيعٌ لَدَيْنَا مُحْضَرُونَ

Za a gabatar da su a gare Mu wata rana!ا

Tafseer

Tafseer

36.35

لِيَأْكُلُوا مِنْ ثَمَرِهِ وَمَا عَمِلَتْهُ أَيْدِيهِمْ ۖ أَفَلَا يَشْكُرُونَ

Dõmin su ci 'ya'yan itãcensa, alhãli kuwa hannãyensu ba su aikata shi ba. Shin, to, bã zã su gõdẽ ba?ا

Tafseer

Tafseer

36.34

وَجَعَلْنَا فِيهَا جَنَّاتٍ مِنْ نَخِيلٍ وَأَعْنَابٍ وَفَجَّرْنَا فِيهَا مِنَ الْعُيُونِ

Kuma Muka sanya, a cikinta ( ƙasã ) , waɗansu gõnaki na dabĩno da inabõbi, kuma Muka ɓuɓɓugar da ruwa daga marẽmari a cikinta.ا

Tafseer

Tafseer

36.37

وَآيَةٌ لَهُمُ اللَّيْلُ نَسْلَخُ مِنْهُ النَّهَارَ فَإِذَا هُمْ مُظْلِمُونَ

Wata ãyã a gare su, ita ce dare: Munã kuranye yini daga bisansa, kuma sunã a cikin duffaiا

Tafseer

Tafseer

36.36

سُبْحَانَ الَّذِي خَلَقَ الْأَزْوَاجَ كُلَّهَا مِمَّا تُنْبِتُ الْأَرْضُ وَمِنْ أَنْفُسِهِمْ وَمِمَّا لَا يَعْلَمُونَ

Tsarki ya tabbata ga Wanda Ya halitta namiji da mace, daga rãyukan ƙasa, daga mutãne, kuma daga abin da ba su sani ba.ا

Tafseer

Tafseer

36.39

وَالْقَمَرَ قَدَّرْنَاهُ مَنَازِلَ حَتَّىٰ عَادَ كَالْعُرْجُونِ الْقَدِيمِ

Kuma da watã, Mun ƙaddara masa marõji, har ya wãyi gari kamar shãshen dabĩno, wanda ya sãke.ا

Tafseer

Tafseer

36.38

وَالشَّمْسُ تَجْرِي لِمُسْتَقَرٍّ لَهَا ۚ ذَٰلِكَ تَقْدِيرُ الْعَزِيزِ الْعَلِيمِ

Kuma rãnã tanã gudãna zuwa ga wani matabbaci nãta. Wancan ƙaddarãwar Allah Mabuwãyi ne, Masani.ا

Tafseer

Tafseer

36.41

وَآيَةٌ لَهُمْ أَنَّا حَمَلْنَا ذُرِّيَّتَهُمْ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ

Kuma ãyã ce a gare su. Lalle Mũ, Mun ɗauki zuriyarsu a cikin jirgin, wanda aka yi wa lõdi.ا

Tafseer

Tafseer

36.40

لَا الشَّمْسُ يَنْبَغِي لَهَا أَنْ تُدْرِكَ الْقَمَرَ وَلَا اللَّيْلُ سَابِقُ النَّهَارِ ۚ وَكُلٌّ فِي فَلَكٍ يَسْبَحُونَ

Rãnã bã ya kamãta a gare ta, ta riski watã. Kuma dare bã ya kamãta a gare shi ya zama mai tsẽre wa yini, kuma dukansua cikin sarari guda suke yin iyo.ا

Tafseer

Tafseer

36.43

وَإِنْ نَشَأْ نُغْرِقْهُمْ فَلَا صَرِيخَ لَهُمْ وَلَا هُمْ يُنْقَذُونَ

Kuma idan Mun so, zã Mu nutsar da su, har bãbu kururuwar neman ãgaji, a gare su, kuma ba su zama anã tsirar da su ba.ا

Tafseer

Tafseer

36.42

وَخَلَقْنَا لَهُمْ مِنْ مِثْلِهِ مَا يَرْكَبُونَ

Kuma Muka halitta musu, daga irinsa, abin da suke hawa.ا

Tafseer

Tafseer

36.45

وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ اتَّقُوا مَا بَيْنَ أَيْدِيكُمْ وَمَا خَلْفَكُمْ لَعَلَّكُمْ تُرْحَمُونَ

Kuma idan aka ce musu, « Ku kãre abin da ke a gaba gare ku da abin da yake a bãyanku, dõmin tsammãninku a ji tausayinku.»ا

Tafseer

Tafseer

36.44

إِلَّا رَحْمَةً مِنَّا وَمَتَاعًا إِلَىٰ حِينٍ

Rahamar mu ce , kuma tana jin dadin rayuwa har zuwa wani ajali ambatacce.ا

Tafseer

Tafseer

36.47

وَإِذَا قِيلَ لَهُمْ أَنْفِقُوا مِمَّا رَزَقَكُمُ اللَّهُ قَالَ الَّذِينَ كَفَرُوا لِلَّذِينَ آمَنُوا أَنُطْعِمُ مَنْ لَوْ يَشَاءُ اللَّهُ أَطْعَمَهُ إِنْ أَنْتُمْ إِلَّا فِي ضَلَالٍ مُبِينٍ

Kuma idan aka ce musu, « Ku ciyar daga abin da Allah Ya azurta ku, » sai waɗanda suka kãfirta su ce ga waɗanda suka yi ĩmãni, « Ashe, zã mu ciyar da wanda idan Allah Ya so Yanã ciyar da shi? Ba ku zama ba fãce a cikin ɓata bayyananniya.»ا

Tafseer

Tafseer

36.46

وَمَا تَأْتِيهِمْ مِنْ آيَةٍ مِنْ آيَاتِ رَبِّهِمْ إِلَّا كَانُوا عَنْهَا مُعْرِضِينَ

Kuma wata ãyã daga ãyõyin Ubangijinsu bã ta zuwa a gare su, sai sun kasance sunã mãsu bijirẽwa daga gare ta.ا

Tafseer

Tafseer

36.49

مَا يَنْظُرُونَ إِلَّا صَيْحَةً وَاحِدَةً تَأْخُذُهُمْ وَهُمْ يَخِصِّمُونَ

Bã su jiran ( kõme ) fãce wata tsãwa guda, zã ta kãma su, alhãli kuwa sunã yin husũma.ا

Tafseer

Tafseer

36.48

وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا الْوَعْدُ إِنْ كُنْتُمْ صَادِقِينَ

Kuma sunã cẽwa, « A yaushe wannan wa'adi yake ( aukuwa ) idan kun kasance mãsu gaskiya? »ا

Tafseer

Tafseer

36.51

وَنُفِخَ فِي الصُّورِ فَإِذَا هُمْ مِنَ الْأَجْدَاثِ إِلَىٰ رَبِّهِمْ يَنْسِلُونَ

To, a lokacin da aka busa a cikin kaho, ya gan su suna fitowa daga kaburbura, suna gudu zuwa ga Ubangijinsu.ا

Tafseer

Tafseer

36.50

فَلَا يَسْتَطِيعُونَ تَوْصِيَةً وَلَا إِلَىٰ أَهْلِهِمْ يَرْجِعُونَ

Bã zã su iya yin wasiyya ba, kuma bã zã su iya kõmãwa zuwa ga iyãlansu ba.ا

Tafseer

Tafseer

36.53

إِنْ كَانَتْ إِلَّا صَيْحَةً وَاحِدَةً فَإِذَا هُمْ جَمِيعٌ لَدَيْنَا مُحْضَرُونَ

Ba ta kasance ba fãce wata tsãwa ce guda, sai gã su duka, sunã abin halartarwa a gare Mu.ا

Tafseer

Tafseer

36.52

قَالُوا يَا وَيْلَنَا مَنْ بَعَثَنَا مِنْ مَرْقَدِنَا ۜ ۗ هَٰذَا مَا وَعَدَ الرَّحْمَٰنُ وَصَدَقَ الْمُرْسَلُونَ

Suka ce: « Yã bonenmu! Wãne ne ya tãyar da mu daga barcinmu? » « Wannan shi ne abin da Mai rahama ya yi wa'adi da shi, kuma Manzanni sun yi gaskiya.»ا

Tafseer

Tafseer

36.55

إِنَّ أَصْحَابَ الْجَنَّةِ الْيَوْمَ فِي شُغُلٍ فَاكِهُونَ

Lalle, 'yan Aljanna, a yau, sunã cikin shagali, sunã mãsu nishãɗi.ا

Tafseer

Tafseer

36.54

فَالْيَوْمَ لَا تُظْلَمُ نَفْسٌ شَيْئًا وَلَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنْتُمْ تَعْمَلُونَ

A rãnar nan bã zã a zãlunce kowa da kõme ba, kuma anã sãka muku da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.ا

Tafseer

Tafseer

36.57

لَهُمْ فِيهَا فَاكِهَةٌ وَلَهُمْ مَا يَدَّعُونَ

Sunã da, 'ya'yan itãcen marmari a cikinta kuma sunã sãmun abin da suke kiran a kãwo.ا

Tafseer

Tafseer

36.56

هُمْ وَأَزْوَاجُهُمْ فِي ظِلَالٍ عَلَى الْأَرَائِكِ مُتَّكِئُونَ

Su da matan aurensu sunã a cikin inuwõwi masu kauri, suna gincire a kan karagu.ا

Tafseer

Tafseer

36.59

وَامْتَازُوا الْيَوْمَ أَيُّهَا الْمُجْرِمُونَ

« Ku rarrabe dabam, a yau, yã kũ mãsu laifi! »ا

Tafseer

Tafseer

36.58

سَلَامٌ قَوْلًا مِنْ رَبٍّ رَحِيمٍ

« Aminci, » da magana, daga Ubangiji Mai jin ƙai.ا

Tafseer

Tafseer

36.61

وَأَنِ اعْبُدُونِي ۚ هَٰذَا صِرَاطٌ مُسْتَقِيمٌ

«Kuma ku bauta Mini. Wannan ita ce hanya madaidaciya. »ا

Tafseer

Tafseer

36.60

أَلَمْ أَعْهَدْ إِلَيْكُمْ يَا بَنِي آدَمَ أَنْ لَا تَعْبُدُوا الشَّيْطَانَ ۖ إِنَّهُ لَكُمْ عَدُوٌّ مُبِينٌ

« Ashe, ban yi muku umurni na alkawari ba, yã ɗiyan Ãdamu? Cẽwa kada ku bauta wa Shaiɗan, lalle shĩ, maƙiyi ne a gareku bayyananne? »ا

Tafseer

Tafseer

36.63

هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي كُنْتُمْ تُوعَدُونَ

« Wannan ita ce Jahannama wadda kuka kasance anã yi muku wa'adi da ita. »ا

Tafseer

Tafseer

36.62

وَلَقَدْ أَضَلَّ مِنْكُمْ جِبِلًّا كَثِيرًا ۖ أَفَلَمْ تَكُونُوا تَعْقِلُونَ

Kuma lalle haƙĩƙa, ( Shaiɗan ) yã ɓatar da jama'a mãsu yawa daga gare ku. Ashe to ba ku kasance kunã yin hankali ba? »ا

Tafseer

Tafseer

36.65

الْيَوْمَ نَخْتِمُ عَلَىٰ أَفْوَاهِهِمْ وَتُكَلِّمُنَا أَيْدِيهِمْ وَتَشْهَدُ أَرْجُلُهُمْ بِمَا كَانُوا يَكْسِبُونَ

A yau, Munã sanya hãtimin rufi a kan bãkunansu, kuma hannãyensu su yi Mana magana, kuma ƙafãfunsu su yi shaidu da abin da suka kasance sunã aikatãwa.ا

Tafseer

Tafseer

36.64

اصْلَوْهَا الْيَوْمَ بِمَا كُنْتُمْ تَكْفُرُونَ

« Ku shigẽ ta a yau, sabõda abin da kuka kasance kunã yi na kãfirci. »ا

Tafseer

Tafseer

36.67

وَلَوْ نَشَاءُ لَمَسَخْنَاهُمْ عَلَىٰ مَكَانَتِهِمْ فَمَا اسْتَطَاعُوا مُضِيًّا وَلَا يَرْجِعُونَ

Idan Mun so, za Mu musanya su a cikin wurarensu, kuma ba za su iya gabatowa ba, kuma ba za su juya baya ba.ا

Tafseer

Tafseer

36.66

وَلَوْ نَشَاءُ لَطَمَسْنَا عَلَىٰ أَعْيُنِهِمْ فَاسْتَبَقُوا الصِّرَاطَ فَأَنَّىٰ يُبْصِرُونَ

Dã Mun so, Mun shãfe gani daga idãnunsu, sai su yi tsẽre ga hanya, to, yaya zã su yi gani?ا

Tafseer

Tafseer

36.69

وَمَا عَلَّمْنَاهُ الشِّعْرَ وَمَا يَنْبَغِي لَهُ ۚ إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ وَقُرْآنٌ مُبِينٌ

Ba Mu sanar da shi wãkã ba, kuma wãkã ba ta kamãta da shi ba. Shi ( Al- ƙur'ãni ) bai zama ba fãce tunãtarwa ce, da abin karãtu bayyananne.ا

Tafseer

Tafseer

36.68

وَمَنْ نُعَمِّرْهُ نُنَكِّسْهُ فِي الْخَلْقِ ۖ أَفَلَا يَعْقِلُونَ

Kuma wanda Muka rãya shi, Manã sunkuyar da shi ga halittarsa. Ashe, bã su hankalta?ا

Tafseer

Tafseer

36.71

أَوَلَمْ يَرَوْا أَنَّا خَلَقْنَا لَهُمْ مِمَّا عَمِلَتْ أَيْدِينَا أَنْعَامًا فَهُمْ لَهَا مَالِكُونَ

Shin, ba su gani ba ( cẽwa ) lalle Mun halitta musu dabbõbi daga abin da HannayenMu suka aikata, sai sunã mallakar su?ا

Tafseer

Tafseer

36.70

لِيُنْذِرَ مَنْ كَانَ حَيًّا وَيَحِقَّ الْقَوْلُ عَلَى الْكَافِرِينَ

Dõmin ya yi gargaɗi ga wanda ya kasance mai rai, kuma magana ta wajaba a kan kãfirai.ا

Tafseer

Tafseer

36.73

وَلَهُمْ فِيهَا مَنَافِعُ وَمَشَارِبُ ۖ أَفَلَا يَشْكُرُونَ

Kuma a cikinsu akwai fa'idodi da abubuwan sha (Madara) a gare su. Shin, bã zã su gõde ba?ا

Tafseer

Tafseer

36.72

وَذَلَّلْنَاهَا لَهُمْ فَمِنْهَا رَكُوبُهُمْ وَمِنْهَا يَأْكُلُونَ

Kuma Sai Muka hõre musu waɗannan, har su hau kan sãshensu, kuma sunã ci naman wasu.ا

Tafseer

Tafseer

36.75

لَا يَسْتَطِيعُونَ نَصْرَهُمْ وَهُمْ لَهُمْ جُنْدٌ مُحْضَرُونَ

Ba za su iya taimakonsu da kome ba, duk da haka mutanen nan sun tsaya a shirye don hidimarsu.ا

Tafseer

Tafseer

36.74

وَاتَّخَذُوا مِنْ دُونِ اللَّهِ آلِهَةً لَعَلَّهُمْ يُنْصَرُونَ

Kuma suka riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa wanin Allah, ɗammãninsu zã su taimake su.ا

Tafseer

Tafseer

36.77

أَوَلَمْ يَرَ الْإِنْسَانُ أَنَّا خَلَقْنَاهُ مِنْ نُطْفَةٍ فَإِذَا هُوَ خَصِيمٌ مُبِينٌ

Shin, kuma mutum bai ga cẽwa lalle Mũ, Mun halitta shi daga ɗigon maniyyi ba, sa'an nan kuma, yanã mai husũma bayyananne?ا

Tafseer

Tafseer

36.76

فَلَا يَحْزُنْكَ قَوْلُهُمْ ۘ إِنَّا نَعْلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعْلِنُونَ

Sabõda haka, kada maganarsu ta ɓãta maka rai. Lalle Mũ, Munã sanin abin da suke asirtãwa da abin da suke bayyanãwa.ا

Tafseer

Tafseer

36.79

قُلْ يُحْيِيهَا الَّذِي أَنْشَأَهَا أَوَّلَ مَرَّةٍ ۖ وَهُوَ بِكُلِّ خَلْقٍ عَلِيمٌ

Ka ce: « Wanda ya ƙãga halittarsu a farkon lõkaci Shĩ ke rãyar da su, kuma Shi, game da kõwace halitta, Mai ilmi ne. »ا

Tafseer

Tafseer

36.78

وَضَرَبَ لَنَا مَثَلًا وَنَسِيَ خَلْقَهُ ۖ قَالَ مَنْ يُحْيِي الْعِظَامَ وَهِيَ رَمِيمٌ

Kuma ya buga Mana wani misãli, kuma ya manta da halittarsa, ya ce: « Wãne ne ke rãyar da ƙasũsuwa alhãli kuwa sunã rududdugaggu? »ا

Tafseer

Tafseer

36.81

أَوَلَيْسَ الَّذِي خَلَقَ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ بِقَادِرٍ عَلَىٰ أَنْ يَخْلُقَ مِثْلَهُمْ ۚ بَلَىٰ وَهُوَ الْخَلَّاقُ الْعَلِيمُ

Shin, kuma wanda Ya halitta sammai da ƙasa bai zama Mai ĩkon yi ba a kan Ya halitta kwatankwacinsu? Me ya sa ba, alhali Shi ne Mahalicci ƙware.ا

Tafseer

Tafseer

36.80

الَّذِي جَعَلَ لَكُمْ مِنَ الشَّجَرِ الْأَخْضَرِ نَارًا فَإِذَا أَنْتُمْ مِنْهُ تُوقِدُونَ

« Wanda ya sanya muku wutã daga itãce kõre, sai gã ku kunã kunnãwa daga gare shi. ».ا

Tafseer

Tafseer

36.83

فَسُبۡحَٰنَ ٱلَّذِي بِيَدِهِۦ مَلَكُوتُ كُلِّ شَيۡءٖ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Tsarki ya tabbata ga wanda ke hannunSa, ikon dukan kõme, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku.ا

Tafseer

Tafseer

36.82

إِنَّمَا أَمْرُهُ إِذَا أَرَادَ شَيْئًا أَنْ يَقُولَ لَهُ كُنْ فَيَكُونُ

UmurninSa idan Yã yi nufin wani abu sai Ya ce masa kawai, « Ka kasance, » sai yana kasancewa.ا

Tafseer

Tafseer

Takaitaccen Suratul Yaseen:

Ana kiran suratu Yaseen da “Zuciyar Alqur’ani”. Ana yawan cewa “Yaseen” kuma sunan Annabi Muhammad (SAW) ne.  Tana da ayoyi 83 kuma ita ce sura ta 36 a cikin Alkur’ani kuma tana da kalmomi 807 da haruffa 3,028. Yana da ruku’u (sections) guda 5. Yana daga cikin Juz’i na 22 kuma ya ci gaba har zuwa Juz’i na 23. An saukar da ita a Makkah, don haka ake kiranta da suratun Makki kuma tana jaddada mahimman abubuwan da ke gaba:

1. Tabbatar da Annabci:

Surar ta fara ne da tabbatar da gaskiyar sakon da Annabi Muhammad (SAW) ya zo da shi. Yana jaddada cewa shi manzo ne da Allah ya aiko domin shiryar da mutane.

2. Alamomin Allah:

Sura ta yi nuni da alamomin samuwar Allah da ikonsa ta hanyar halitta. Ya ambaci canjin dare da rana, da tsirowar tsiro, da abubuwan al’ajabi na duniya, yana ƙarfafa mutane su yi tunani a kan waɗannan alamu a matsayin shaida na girman Allah.

3. Karyata Sakon:

 Yana magance taurin waɗanda suka ƙaryata saƙon. Duk da bayyanannun alamu da mu’ujizai da aka nuna musu, da yawa sun ci gaba da ƙin gaskiya, wanda hakan ya kai ga ukubarsu da babu makawa.

4. Misalai na Al’ummai da suka gabata:

Surar ta ba da labarin al’ummomin da suka yi watsi da annabawansu kuma suka fuskanci halaka a sakamakon haka. Wannan ya zama gargaɗi ga waɗanda suka ƙaryata.

5. Tashin Kiyama da Lahira:

Suratul Yaseen ta yi bayani kan haqiqanin tashin qiyama da rayuwa bayan mutuwa. Ya nanata cewa za a ta da dukan ’yan Adam a Ranar Ƙiyama, inda za a yi musu hisabi game da abin da suka yi.

6. Rahamar Allah:

Surar tana tabbatar wa masu imani rahamar Allah da lada ga wadanda suka karbi sakon. Yana nuna bambanci tsakanin makomar salihai da kafirai, yana mai jaddada cewa muminai za su dawwama a cikin aljanna.

7. Kira don Tunani:

Surar ta kare ne da kwadaitar da mutane da su yi tunani a kan rayuwarsu, da ayoyin Allah da ke kewaye da su, da kuma hakikanin gaskiyar tashin kiyama da hisabi.